Gabatarwa

 بسم الله الرحمن الرحيم

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI

MU MUNA BAYAR DA MAFI KYAWUN LABARAI A GARE KA

SURATU YUSUF AYA TA 3


 

Godiya ta tabbata ga Allah amincinsa ya tabbata ga bayinsa zababbu Annabi Muhammadu da yayan gidansa, Imamai ma asumai masu albarka.

Rayuwar Imamai maasumai (A.s.) ta taro falala da Kuma dabiu na kwarai don kuwa sune masu shir ya swa ga bil Adama kuma sune masu kira zuwa ga alheri sabili da haka Allah Madaukaki ya zabe su domin su zama shugabanni kuma ababen koyi ga mutane.

Hakika tarihinsu ya kunshi labarai na koli wanda ke nuna muhimmancin halaye da kuma dabiu na gari a rayuwar al ummu.

To don ganin cewa tarihin rayuwarsu mai albarka yana da yawa so sai sai Muassasar Imam Ali (A.s.) ta fara buga tarihinsu a jere ta hanyar da ta dace da matasa. Sai ta zabo wani lamari daga rayuwar su ta buga shi wani lamari daga rayuwar su ta buga shi a salon labari, an kuwa zabi wannan hanyar ce domin a ga amfanin dake cikin rayuwarsu ya game kowa, kuma daga bisani a kwadaitar da ya yanmu domin su kara Samun ilimi da kuma ci gaba na ruhi wanda tarihin musulana madauwami ya kunsa.

Muna rakon Allah madaukaki mai iko yayi mana katari ga abinda zai zama hidima ga tarihin Ahlul Bait tsarkakku.

DUKKAN HAKKW MALLAKA YA RATAYA GA:   MUASSASAR IMAM ALI (A.S.)

 

 Allah shi ne mai yin katari.

Muassasar Imam Ali (A.s.)

Watan shauwal

1418 Hijiriyya. 

عنوان الکتاب